Nigerian Army arrests Boko Haram suspect, others in Taraba

Troops of the 6 Brigade Nigerian Army/Sector 3 Operation Whirl Stroke, OPWS, have apprehended a suspected Boko Haram terrorist and others involved in the kidnapping of a district head in Taraba State.
The alleged Boko Haram member, identified as Nura Yakubu, was arrested on December 20, 2024, in Garba Chede, Bali Local Government Area.
According to a statement issued to journalists on Friday in Jalingo by the Acting Spokesperson of the Brigade, Captain Oni Olubodunde, the suspect was a food vendor who reportedly harbored Boko Haram operatives deployed to Taraba State for terrorist activities.
“Investigations further linked Yakubu and his gang to previous kidnappings in the area, including those of a businessman, Mr. Arinze, and the son of Alhaji Ibrahim in Garbatau,” the army said.
In a separate operation, the army also announced the arrest of Musa Suito on December 18, 2024, in Jalingo for his alleged involvement in the kidnapping of a district head on November 27.
Suito, a member of a vigilante group, was alleged to have exploited his position to gather intelligence for kidnappers in the state.
Items recovered from him included a dane gun and two cartridges.
The Brigade Commander, Kingsley Uwa, expressed the army’s commitment to safeguarding lives and property in Taraba State.
He urged residents to remain vigilant and cooperate with security agencies by providing timely and credible information to combat criminal activities effectively.
Nigerian Army arrests Boko Haram suspect, others in Taraba

Gwamnan Kano ya nuna gamsuwa da kokatin wakilan Kano a Musabakar Alkur’ani

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana gamsuwa da yadda wakilan jihar Kano suka gudanar karatu a musabakar alqur’ani mai girma ta kasa karo na 39 wadda take gudana yanzu haka a jihar Kebbi.
Gwamnan ya bayyana hakan ne ta bakin mai bashi shawara na musamman kan harkar tsangaya Gwani Musa Falaki lokacin da yake ganawa da manema labarai a jihar ta Kebbi.
Gwamnan yace wakilan na jihar Kano sun cancanci yabo duba da yadda suka yi karatu a matakai daban-daban tare da amsa tambayoyi daga alkalan gasar cikin kwarewa ba tare da kuskure ba.
Ya kuma yi alkwarin karrama wakilan na Kano da zarar sun dawo gida domin karfafa musu gwiwa, tare da tabbata da ganin andaga darajar malaman daliban da kyautata walwalar su.
Gwamnan Kano ya nuna gamsuwa da kokatin wakilan Kano a Musabakar Alkur’ani

Gwamnatin Sokoto zata binciki harin da jirgin yaki ya kai wasu kauyuka

Gwamnan jihar Sokoto, Ahmad Aliyu, ya ce gwamnatinsa za ta gudanar da bincike kan abin da ya janyo harin kuskure na jiragen saman sojin ƙasar wanda ya kashe farar-hula 10 tare da kashe dabbobi a ƙauyukan Gidan Bisa da Runtuwa da ke ƙaramar hukumar Silame.
Wata sanarwa da Sakataren Watsa Labarai na jihar Sokoto, Abubakar Bawa, ya fitar ta ambato gwamnan yana bayyana lamarin a matsayin “abin takaici.”
Rahotanni dai sun ce an tafka kuskuren ne yayin da dakarun ƙasar nan ke ƙoƙarin fatattakar Lakurawa ‘yan ta’adda a jihar.
Gwamnatin Sokoton tace za ta bai wa ‘yan’uwan waɗanda lamarin ya rutsa da su kyautar naira miliyan 20 da kuma buhu hatsi 100 tare da biya kuɗin kulawa da waɗanda suka ji rauni a harin a asibiti.
Wannan ba shi ba ne karon farko da aka samu irin wannan harin da soji suka afka wa farar-hula bisa kuskure a Nijeriya ba.
Ko a ranar uku ga watan Disamban bara (2023) ma, an kai harin jirgi mara matuki a wani taron Maulidi da ake a ƙauyen Tudun Biri da ke jihar Kaduna inda aka kashe kimanin mutum 88.
Gwamnatin Sokoto zata binciki harin da jirgin yaki ya kai wasu kauyuka

Yan sandan Kano sun kama matashin daya haddasa rikicin daba

Rundunar ‘yan sanda anan Kano ta sanarda kama wani matashi bisa zargin kitsa rikicin da ya ɓarke tsakanin ’yan daba na Kofar Mata da matasan Zango da ya faru kwanan nan.
Matashin mai suna Kabiru Jamilu mai shekara 21, mazaunin rukunin gidaje na Zango Quarters an kamashi ne Unguwar Kofar Mata kusa da Asibitin kwararru na Murtala Mohammed.
A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sanda anan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, ya ce wanda ake zargin ya amsa laifin jagorantar faɗan da aka yi.
Kiyawa ya ci gaba da cewa, binciken ne ya kai ga kama Umar Garba mai shekara 32, mazaunin Zango, wanda aka same shi da wata doguwar wuƙa mai kaifi.
Tuni dai an miƙa waɗanda ake zargin zuwa sashin binciken manyan laifuka na rundunar kuma za a gurfanar da su gaban kotu bayan kammala bincike.
Idan za’a iya tunawa dai rikicin daban da akayi kwanakin baya da ya janyo asarar rayuka da raunata wasu, kuma ya yi sanadin asarar kadarorin jama’a da dama a yankin.
Yan sandan Kano sun kama matashin daya haddasa rikicin daba

Najeriya ta fice daga cikin sunayen kasashe Afrika goma da akafi bin bashi – IMF

Wani sabon rahoto da asusun bayar da lamuni ta Duniya (IMF) ta fitar ya nuna Najeriya bata cikin ƙasashen Afrika da aka fi bi bashi a shekarar 2024.
Rahoton ya nuna cewa a tsakanin watan Janairu zuwa Yuni na wannan shekarar, gwamnatin tarayya ta biya sama da Dala biliyan 2.24 na basussukan da ake bin ta wanda ya fitar da ita daga ƙasashen da bashi ya yi musu katutu.
Rahoton da ofishin kula da basussuka na Nijeriya ya fitar ya nuna cewa a watanni 3 na farkon 2024, gwamnatin ta biya dala biliyan 1.12 na bashin da ake bin ta.
A watanni 6 na shekarar ne kuma ta sake biyan Dala biliyan 1.12 ga ƙasashe da kuma hukumomin da ke bin ta bashi da suka haɗa da IMF da Babban Bankin Duniya.
Rahoton ya bayyana ƙasar Misira a matsayin wacce take da mafi girman kaso a Nahiyar da ya zarce Dala biliyan 9.
Najeriya ta fice daga cikin sunayen kasashe Afrika goma da akafi bin bashi – IMF

Despite challenges, Lord’s Chosen continues to grow – Muoka

Pastor Lazarus Muoka of the Lord’s Chosen Charismatic Revival Movement (a.k.a. Chosen) has stated the church is planning to expand its footprints in the country amid challenging times. Muoka stated this on Thursday at a thanksgiving service at the church’s headquarters, Ijesha, Lagos. The News Agency of Nigeria reports that the service featured praise/worship, deliverance,
Read More